1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan Boko Haram na samun horonsu ne a Somaliya

Kamaluddeen SaniFebruary 14, 2016

A dai-dai lokacin da ake kammala taron tsaro na kasa da kasa a birnin Munich na Jamus, Shugaban kasar Somaliya Hassan Sheikh Mahmud ya ce mayakan Boko Haram na samun horo ne a Somaliya.

https://p.dw.com/p/1HvMd
München Sicherheitskonferenz - Hassan Sheikh Mohamud, Präsident Somalia
Hoto: Reuters/M. Dalder

Shugaban kasar Somaliyan ya kara da cewar mayakan na samun horon ne kafin daga bisani su wuce kai tsaye zuwa kasar da ke a yammacin Afrika.

Ya ce fadawa rikita-rikitar siyasa da cin hanci da hare-haren da kungiyar Al-Shabaab ke kaiwa a kasar babu kakkautawa shi ne musabbabin rashin samun cigaba a kasar.

Kazalika ya kara da cewar rashin samun zaman lafiya a Somaliya, tamkar daukacin yankin yana cikin halin rashin tabbas ne gami da daukacin nahiyar Afrika, a inda ya ce tabbas akwai shaidun da suke nuni da cewar 'yan Boko Haram na samun horonsu ne daga Somaliya.

Shugaban Somaliyan na wadannan kalaman ne a lokacin da ake kokarin kammala babban taron tsaro da jami'an tsaro gami da ministocin harkokin kasashen duniya a birnin Munich a inda mahalarta taron suka tattauna batutuwan tsaro da Siriya da kwararar 'yan gudun hijira.