1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hariri ya janye takardar murabus dinsa

Ahmed Salisu
December 5, 2017

Firaministan Lebanon Sa'ad Hariri ya bayyana a wannan Talatar cewar ya janye takardar murabus dinsa da ya gabatar a watan jiya bayan da ya fice daga kasar zuwa Saudi Arabia.

https://p.dw.com/p/2onLo
Libanon Saad Hariri
Hoto: Getty Images/AFP/J. Eid

Hariri ya aike da wannan sako ne ga majalisar ministocin kasar lokacin da ya ta yi zamanta na farko tun bayan da ya koma kasar makonni biyun da suka gabata. Majalisar ta dai ta nuna jin dadinta da wannan matakin da Firaministan ya dauka. Hariri dai ya ce ya yanke hukuncin cigaba da aiki a matsayinsa na jagoran gwamnatin kasar ne in har kungiyar nan ta Hezbolla da ke samun goyon bayan Iran za ta dakatar da yin shisshigi a harkokin siyasar yankin musamman ma dai a kasar Siriya da Yemen.