1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin kunar bakin wake a kasar Pakistan

November 15, 2005
https://p.dw.com/p/BvL8

Hukumomin yan sanda a kasar Pakistan sun sanar da aukuwar fashewar bom a wani dakin cin abinci a birnin karachi wanda ya yi sanadiyar mutuwar a kalla mutane shida da jikata wasu da dama. Baturen yan sanda na birnin Karachi Mushtaq Shah ya baiyana fashewar bom din wanda aka dasa a cikin wata yar karamar mota da cewa hari ne na taáddanci wanda aka kitsa domin haddasa mummunan barna. Babu wata kungiya da ta baiyana daukar alhakin kai wannan harin.