Harin Isra’ila ya janyo asarar rayukan Falasɗinawa 11.
June 14, 2006Talla
A wata sabuwa kuma, Falasɗinawa 11 ne suka rasa rayukansu, sa’annan wasu 30 kuma suka ji rauni, sakamakon wani harin da jiragen saman yaƙin Isra’ila suka kai kan guraban Falasɗinawan a zirin Gaza. Ƙungiyar ’yan ta kifen nan ta Islamic Jihad, ta ce mayaƙanta biyu na cikin waɗanda suka rasa rayukansu a harin. Sa’o’i kaɗan kafin wannan harin dai, sai da wasu dakarun Isra’ilan suka bindige wani ɗan ƙungiyar nan ta baraden al-Aqsa, a wata musayar wutar da suka yi a garin Jenin da ke Gaɓar Yamma.
Jami’an leƙen asirin Isra’ilan, sun kutsa cikin wani asibiti ne a garin, don su cafke mutumin, wanda suke nema kamar ruwa a jallo, yayin da musayar wutar ta ɓarke.