1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin Bomb ya kashe mutane 8 a Najeriya

August 5, 2012

Wani ɗan kunar baƙin wake cikin mota ya kai hari akan sojojin dake binciken ababan hawa, a garin Damaturu jihar Yobe inda ya kashe sojoji shida da fararen hula biyu.

https://p.dw.com/p/15kNO
epa03259333 Nigerians look at the remnants of a suicide bombers vehicle at the Christ Chosen Church of God Rukuba following the bomb blast the previous day in Jos, Nigeria, 11 June 2012. At least two churches were hit by attacks in Nigeria on 10 June 2012, leaving at least two dead and several wounded, officials confirmed. At least five people were injured when gunmen opened fire, spraying bullets into the congregation of a church in the town of Biu in Borno state. Police said scores were injured and a woman died. In a separate attack in the central state of Jos, a suicide blast hit churchgoers at around 11 am as they left a Sunday service, officials said. EPA/STR +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: picture-alliance/dpa

Duk da cewar babu wanda ya ɗauki alhakin wannan harin, ana zargin ƙungiyar Ahalil sunnah lidda'awati wal jihad da aka fi sani da suna Boko Haram da kai harin. Commissionan 'yansanda na jihar Yobe, Patrick Egbmuniwe ya sanar da cewar, ɗan ƙunar baƙin waken ya tayar da boma-boman da yake ɗauke da su ne, kafin a tsayar da motar da yake ciki. Nan take sojoji shida suka mutu, da wani farar hula. Wani lokaci bayan nan ne, mutum na takwas ya rasa ransa asibiti, sakamakon rauni daya samu daga harin. Amurka dai ta ayyana ƙungiyar ta Boko haram, a matsayin ɗaya daga cikin kungiyoyin tarzoman kasa da kasa, wadda kuma keda alhakin hare-hare masu yawa da ake kaiwa a yankunan arewacin Najeriya. Wani Mazaunin unguwar gidajen gwamnati na Shagari dake Damaturu, inda aka kai harin Abdullahi Sabo, ya ce unguwar gaba ɗaya ta girgiza sakamakon karfin tarwatsewar bomb ɗin. A yanzu haka dai wasu jami'in sojin na karɓar jinya a asibiti, daga raunin wannan harin.

Mawallafiya: Zainab Mohammed Abubakar
Edita : Abdullahi Tanko Bala

.