1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hare-haren Isra´ila a zirin Gaza

August 31, 2006
https://p.dw.com/p/Bul6
Wolfgang Tiefensee, ministan sufuri da ayyuka da raya birane na tarayyar Jamus.
Wolfgang Tiefensee, ministan sufuri da ayyuka da raya birane na tarayyar Jamus.Hoto: AP

Shugaban hukumar Palestinawa Mahamud Abbas, yayi kira ga ƙasashen dunia, da su tsawatawa Isra´ila, ta dakatar da kai hare hare, zuwa yankunan Palestinu.

Abbas ya jaddada wannan kira bayan da rundunar Isra´ila ta hallaka wasu fara hulla guda 9 da basu san hawa ba balle sauka.

A ɗaya hannun kuma, ya gayyaci yan yaƙin sunƙurun Palestinu, su daina harba rokoki daga zirin Gaza, zuwa Isra´ila, domin a cewar sa, hakan ya zama aibu, ga zaman lahia da kwanciyar hankali a cikin kasa.

Saidai ɓangarorin 2, sun yi buruss da wannan kira, domin ko a sahiyar yau, Isra´ila ta kai wani samame a yankin Naplouse, wanda ya yi sanadiyar mutuwar Fadi Qafishey shugaba dakarun Al-Aqsa.

A dangane da halin da ake ciki a zirin Gaza, mataimakin sakaren hukumar bada agaji ta Majalisar Dinkin Dunia, Jean Egeland, ya ja hankalin Majalisar, bisa mahimancin duba wannan matsala da idon basira.