Gwamnatin Somalia ta shawo kan rikicin Mogadishu
April 26, 2007Talla
P/M Somalia Ali Mohammed Gedi ya sanar da cewa dakarun sojin gwmnati sun sami nasarar fatafakar yan Islama a birnin Mogadishu, bayan ɗauki ba daɗi da aka kwashe tsawon kwanaki tara ana gwabzawa. Yace a yanzu an shawo kan dukkan wata tarzoma a birnin, sai dai rahotanni sun baiyana cewa an jiwo amon harbin bindigogi dana igwa a kudancin birnin na Mogadishun. P/M Gedi yace yan Somaliya su kimanin 340,000 waɗanda suka yi ƙaura daga gidajen su sakamakon kazamin faɗan mafi muni da aka taba gani a birnin tun shekaru 15 da suka wuce, a yanzu suna iya komawa gida. Bugu da ƙari yace sojojin gwamnati da aminan su na ƙasar Habasha sun kame wani yanki mai girma na yan tawayen a arewacin Mogadishu yana mai cewa yan tawayen fiye da 100 suka miƙa wuya.