1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gwamnatin riƙon ƙwarya ta ƙasar Kirgistan ta soke zaɓen shugaban ƙasa

May 19, 2010

Hukumomi a ƙasar Kirgistan sun bada sanarwa cewa an soke zaɓen shugaban ƙasar da aka shirya gudanarwa a cikin watan oktoba

https://p.dw.com/p/NSFS
Fadar majalisar dokoki ta ƙasar KirgistanHoto: picture-alliance / Bildagentur-online/McPhoto-Str

 Gwamnatin riƙon kwarya a ƙasar Kirgistan ta soke zaɓen shugaban ƙasa da aka shirya gudanarwa a cikin watan oktba, tare da naɗa Mista Rosa Otounbaieva a masayin shugaban ƙasa har zuwa ƙarshen shekara ta 2011.

Nan gaba ne dai a cikin watan yuni za a tabbatar da naɗin ta hanyar yin ƙuria'ar jin ra'ayin jama'a da kuma tantance sabon kundin tsarin mulki na ƙasar.

Gwamnatin wucin gadin, wacce ta karɓi mulki a cikin watan aprilu, bayan wani bore da ya kada gwamnatin Kourmanbek Bakiev, ta sheda cewar a cikin watan oktoba zaɓen 'yan majalisar dokoki kaɗai za a gudanar

Mawallafi: Abdourahamane Hassane

Edita       :  Ahmad Tijani Lawal