1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gwamnatin Iraki tana neman kawo karshen IS

February 19, 2017

Gwamnatin Iraki ta kaddamar da farmakin kwace yammacin birnin Mosul daga hannun mayakan IS, lamarin da ke zama matakin karshe na tarwatsa tsagerun.

https://p.dw.com/p/2Xqto
Irak Mossul Offensive der Regierungstruppen gegen IS
Hoto: Getty Images/AFP/A. Al-Rubaye

Firaminista Haider al-Abadi na Iraki ya bayyana cewa sojoji sun kaddamar da farmaki domin kwace yammacin birnin Mosul daga hannun tsagerun kungiyar IS. Hakan ya zo watanni hudu bayan sojojin sun farma birnin da ke zama tungar karshe na tsagerun na IS.

Kwace yammacin birnin Mosul zai zama wani aiki mai wahala saboda yadda masu ikirarin jihadi suka mamaye yankin, inda tuni aka kara yawan jami'an tsaro domin tabbatar da samun nasarar dakarun Iraki a wannan gagarumin aiki.