1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gwamnati Zambiya ta cafke 'yan jarida

Suleiman BabayoJune 28, 2016

Mutane uku da gwamnati Zambiya ta cafke sun hada da 'yan jarida biyu bayan rufe jadiyar Post.

https://p.dw.com/p/1JFDs
Sambia Protest gegen Schließung von Zeitung in Lusaka
Hoto: picture-alliance/AP Photo/M. Mwape

'Yan sanda a kasar Zambiya sun tuhumi muitane uku da suka hada da 'yan jarida biyu, wadanda aka rufe gidan jaridar da suke aiki saboda sun shiga gidan jaridar da aka rufe. Jaridar ta kasance mai sukar gwamnatin kasar, yayin da ake kara zaman zullumi bisa zaben kasa baki daya na watan Agusta mai zuwa.

Hukumar tara kudaden shiga ta rufe jaridar Post a makon jiya saboda rashin biyan kudaden haraji na dala milyan shida, amma jaridar ta zargi gwamnatin ta Zambiya da neman rufe bakin masu adawa da ita, sannan ta kara da cewa dokar ta aka yi aiki da ita tana gaban kotu, saboda akwai takaddama.

Tuni Shugaba Edgar Lungu na kasar ta Zambiya ya kare matakin hukumar tara kudaden shigar. 'Yan jarida suna zargin gwamnati ta dauki matakin domin rufe bakin masu adawa da ita.