1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gwamman mutane ne suka halaka a Yemen

October 19, 2016

A na dai kokari na kawo karshen zubar da jini a wannan kasa tun bayan shigar Saudiyya a watan Maris na shekarar 2015 dan tallafa wa gwamnatin Shugaba Abedrabbo Mansour Hadi.

https://p.dw.com/p/2RRh4
YEMEN-CONFLICT-SANAA-STRIKES
Hoto: AFP/Getty Images

Rikici da ya barke a tsakanin mayaka a Yemen gabannin tattaunawar zaman lafiya da Majalisar Dinkin Duniya ke shiga tsakani a wannan Laraba ya yi sanadi na kisan gwamman mayakan da ke shan matsin lamba na su rungumi matakan zaman lafiya dan kawo karshen shekaru biyu na yakin basasar da kasar ta fada.

Shirin yarjejeniyar dai na zama karo na shida a kokari na kawo karshen zubar da jini a wannan kasa tun bayan shigar Saudiyya a watan Maris na shekarar 2015 dan tallafa wa gwamnatin Shugaba Abedrabbo Mansour Hadi bayan da 'yan tawayen suka mamayi yankuna da dama na Yemen.

Fararen hula dai da dama sun halaka a yakin da wannan kasa ta Yemen ta fada wanda ya lakume rayukan mutane 6,900 sama da rabin adadin da ke zama fararen hula.