1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gobara ta hallaka mutane 70 a Mozambik

November 18, 2016

Gobarar ta tashi lokacin da babbar mota tankar mai ta kama da wuta abin da ya hallaka fiye da mutane 70 cikin yankin tsakiyar kasar Mozambik.

https://p.dw.com/p/2SrxX
Mosambik Filipe Nyusi
Hoto: DW/B. Jequete

Fiye da mutane 70 sun hallaka sakamakon gobarar da ta tashi lokacin da mota tankar mai ta kama da wuta a yankin tsakiyar kasar Mozambik. Kafofin yada labarai na kasar sun ce akwai kimanin mutane 100 da suka samu raunika, kuma akwai yara a ciki.

Mahukunta sun kaddamar da binciken sanin ko ana sayar da man ne lokacin da lamarin ya faru, ko kuma mazauna yankin ne suka yi wa motar kwantan bauna. Tuni gwamnatin kasar ta Mozambik ta tura ministoci uku zuwa wajen da aka samu gobatar domin gani da ido da sanin hakikanin abin da ya faru.