1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Girgizar kasa mai karfi ta afku a Indunisiya

Abdul-Raheem Hassan/ MABDecember 9, 2015

Wannan bala'in ya Saba afkuwa a Indunusiya. Amma kuma a wannan karon babu fargabar igiyar ruwan Tsunami bayan girgirzar kasa a mashigin ruwan Banda.

https://p.dw.com/p/1HKBG
Bildergalerie größte Naturkatastrophen weltweit
Hoto: AFP/Getty Images/Choo Youn Kong

Wata girgizar kasa da ta kai karfin maki bakwai a ma'aunin Richter ta afku a mashigin ruwan Banda Aceh da ke kasar Indonusiya. Ba a dai bayyana yawan mutane da suka rasa rayukansu ko kuma dukiya da ta lalace ba i zuwa yanzu. Sai dai kuma hukumomin Indunusiya sun bayyana cewar babu fargabar afkuwar ingiyar ruwan Tsunami

Ita dai Indunusiya ta saba fuskantar bala'in girgizar kasa mai karfin gaske, inda a shekara ta 2004 mutane dubu 170 suka rasa rayukansu sakamakon girgizar kasa hade da igiyar ruwan Tsunami.