1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Girgizar kasa a lardin Aceh na Indunisiya

December 7, 2016

An ba da rahoton cewar akalla mutane guda 25 suka rasa rayukansu kawo yanzu bayan wata girgizar kasar da ta afku a arewacin kasar Indunisiya.

https://p.dw.com/p/2TsJq
Indonesien Erdbeben in Aceh
Hoto: picture alliance/AP Photo/H. Juanda

Girgiza kasar mai karfin maki shida da digo hudu da ta kada a lardin na Aceh da ke a arewacin tsibirin Sumatra ta rigito da gidaje da dama,kuma yanzu haka masu aikin ceto na can na  ci gaba da aikin zakulo jama'ar da suka makale a cikin kuraguzan gine-ginen

Lardin dai na Aceh a shekara ta 2014  na daga cikin yankunan da guguwar Tsunami ta hadassa mumanar barna.