1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ghana: Ana cigaba da kidayar kuri'u

Ahmed Salisu
December 8, 2016

Hukumar zaben Ghana na cigaba da kidaya kuri'un zaben shugaban kasa da na 'yan majalisa wanda aka gudanar ranar Larabar da ta gabata a fadin kasar.

https://p.dw.com/p/2TvNX
Ghana Wahlen Abstimmung Auszaehlung Warten
Hoto: AP

Masu ruwa da tsaki a harkokin zaben na Ghana sun ce suna cigaba da kidaya kuri'un da aka kada a zaben shugaban kasa wanda fafatawa ta fi zafi tsakanin shugaba mai ci John Mahama na jam'iyyar NDC da kuma babban mai hamayya dantakarar jam'iyyar NPP mai adawa Nana Akufo-Addo. Rahotanni sun bayyana cewa ana kidayar lami lafiya kuma ya zuwa yanzu ba wani labari daga hukumar zaben kasar kan wanda ke kan gaba a wannan kidaya da ake yi. A ranar Asabar din da ke tafe ne dai ake sa ran samun cikakken sakamakon. Idan har ba dan takarar da ya samu fiye da kashi 50 cikin 100 to dole a tafi zagaye na biyu a zaben.