1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gangamin adawar ficewar Birtaniya daga EU

Ramatu Garba Baba
September 9, 2017

Dubban 'yan kasar Birtaniya ne suka gudanar da wani gangami na nuna adawa da matakin kasar na ficewa daga cikin kungiyar tarayyar Turai ta EU bayan kuri'ar raba gardama da aka kada a bara kan wannan batu.

https://p.dw.com/p/2je4h
People´s March for Europe London
Hoto: Imago

Shahararrun mawakan Birtaniya da wasu manyan 'yan siyasa sun shiga cikin gangamin na birnin London inda suka fantsama kan tituna suna tattaki har zuwa ginin majalisar kasa.

Masu gangamin da dama sun sanya riguna masu launin tutar EU yayin da wasu ke rike da tutar kungiyar, wasu kuwa na dauke da alluna da rubuce rubuce na adawa da ficewar Birtaniya daga EU.

Gangamin na ranar Asabar na zuwa ne a yayin da a ranar Litinin majalisar ke shirin kada kuri'a kan matakin kasar na ficewa baki daya daga cikin kungiyar ta EU.

Akalla mutane dubu hamsin ne suka shiga wannan gangami.