Ganawar Trump da Buhari
April 30, 2018Talla
Donald Trump ya gayyaci shugaba Muhammdu Buhari na Najeriya zuwa fadar White House, inda ake sa ran za su tattauna batutuwa da suka shafi yaki da ayyukan ta'addanci da kuma bunkasa tattalin arzikin kasa.
Trump ya sasha suka daga al'umma bayan da ya baiyana kasashen nahiyar Afirka a matsayin wulakantatu duk da cewa daga baya ya janye kalaman da ya ce rashin fahintarsa aka yi don kuwa ba hakan ya ke nufi ba.