Ganawa tsakanin alummar musulmi da jamian gwamnatin Jamus
September 27, 2006Talla
Wakilai daga alummomin musulmi 15 dake nan Jamus sun gana karo na farko da jamian gwamnatin Jamus a birnin Berlin.
Wannan dai shine karo na farko a jerin tattaunawa da aka shirya zaa rika gudanarwa tsakanin gwamnati da alummar musulmin Jamus cikin shekaru 2 zuwa 3 masu zuwa,tare da nufin mahawara kan batutuwa da suka shafe su.
Ministan harkokin cikin gida na kasar Jamus Wolfgang Schäuble shi ya jagoranci tattaunawar,wadda akayi akan batutuwa kamar matsayin mata a musulunci da kuma alaka dake tsakanin gwamnati da addini.