1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gambiya ta bayyana shirin fita daga kotun duniya

October 26, 2016

Gambiya ta bi sahun kasashen Afirka ta Kudu da Burundi wajen neman fita daga kotun duniya mai hukunta manyan laifukan yaki.

https://p.dw.com/p/2Rjur
Elfenbeinküste Präsident Yahya Jammeh in Yamoussoukro
Hoto: Getty Images/AFP/I. Sanogo

Kasar Gambiya ta zama kasa na baya-baya cikin kasashen Afirka da suka nuna bukatar ficewa daga cikin kotun duniya mai hukuntan manyan laifukan yaki, inda ta zargi kotun da musguna wa 'yan Afirka, kamar yadda ministan shari'a na kasar Sheriff Bojang ya sanar da gidan talabijin na gwamnati. Matakin kasar da ke yankin yamamcin Afirka yana zuwa bayan kasashen Afirka ta Kudu da Burundi sun bayyana matakin watsi da kotun ta duniya cikin wannan wata na Oktoba da muke ciki.

Matakin na Gambiya zai iya shafi kotun mai mazauni a birnin Hague na kasar Holland, saboda babbar mai gabatar da kara a kotun Fatou Bensouda ta kasance 'yar kasar ta Gambiya. Matakin gwamnatin Gambiya ya zo makonni kafin zaben shugaban kasa na ranar daya ga watan Disamba mai zuwa, inda Shugaba Yahya Jameeh yake rike da madafun iko tun shekarar 1994 bayan juyin mulki na sojoji.