1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Firaministan Palasdinu ya musanta dakatar da tattaunawar kafa gwamnatin hadaka

September 17, 2006
https://p.dw.com/p/BujD

Firaministan Palasdinawa Ismail Haniyeh ya musa cewa shugaban Palasdinawa Mahmud Abbas ya dakatar da tattaunawar kafa gwamnatin hada a yankin.

Haniyeh yace,an jingine tattaunawar ce saboda Abbas zai hakarci tarukan Majalisar Dinkin Duniya ne cikin wannan mako.

Tun farko a yau masu baiwa shugaban na Palasdinwa shawar sun sanarda cewa,an dakatar da tattaunawar saboda kungiyar Hamas mai mulki ta janye daga sharuddan yarjejeniyar kafa gwamnatin hadaka.

Haniyeh ya fadawa manema labaru cewa,sun shirya tare da Abbas cewa zasu ci gaba da tattaunawa da zarar Abbas din ya komo daga taron na Majalisar Dinkin Duniya.