Farkon azumin watan Ramadan
September 13, 2007Saɓanin Taraya Nigeria, Jamhuriya Niger, da Lybia, da su ka fara azumin watan Ramadan tun jiya, a yau ne mafi yawan ƙasashe muslunci na dunia su ka daujki azumin farko.
A ƙasar Indonesia da ta fi yawan muslmi a dunia, an fara azumin na shekara bana cikin halin juyayi, a sakamakon girgiza ƙasar da ta abku a jiya laraba, wada kuma ta hallaka a ƙalla mutane 10.
A ƙasar Bangladesh gwamnati ta bayyana dokar rage parashen kayan masarufi, albarkacin watan mai tsarki, da kashi 20 cikin ɗari.
Kazalika, a kussan dukan ƙasashen larabawa, a yau ne a ka fara gudanar da ibadar wattan ramadan.
A Irak da ke fama tashe-tahen hankula dakarun Amurika sun bayyana aniyar sako pirsinoni masu yawa a cikin wannan wata.
A nasu ɓangare, ƙasashen Marroko da Senegal, da kuma yan ɗarikar Schi´a, na Iran da Irak sun yanke shawara fara azumin gobe juma´a.