1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fargaba kan sabbin hare-haren a yankin Niger-Delta

Uwaisu Abubakar Idris/GATMay 9, 2016

A Najeriya sabbin hare-hare kan na'urorin hako mai a yankin Niger-Delta a dai dai lokacin da shugaban kasar ya sanya hannu kan kasafin kudi ya haifar da damuwa kan illar da wannan zai iya yi ga aiwatar da kasafin kudin.

https://p.dw.com/p/1IkjN
Nigeria Port Harcourt Arbeiter auf Plattform Ölförderung
Hoto: Getty Images/AFP/P. Utomi Ekpei

Hare-haren har sau biyu da aka kai a kan naurorin tura man fetir da ke nuna kama hanyar sake komawa ga kai hare-hare a kan harakar man fetur din tun bayan afuwar da gwamnatocin da suka gabata suka yi wa masu wannan aika-aika a yankin na Niger-Delta ya zama abin da ke tayar da hankali da tsoron sakamakon da zai iya samuwa ga sashin man Najeriyar.

Niger Kämpfer
Hoto: picture-alliance/dpa

Ana dai danganta wadannan hare-hare na baya-bayan nan da neman kame daya daga cikin madugun kungiyoyin da ke tada kayar baya a yankin watau Tompolo da gwamnatin Buhari ke yi bisa zargin cin hanci da rashawa.

Sanin yadda Najeriya ta dogara kusan kacokam a kan man fetir a matsayin hanyar samun kudin shigarta da zai zama abin dogaro a yanzu ga gwamnatin da ke kukan rashin kudin da raguwar farashin man, tuni ya sanya nuna damuwar yadda kai tsaye zai iya shafar aiwatar da kasafin kudin kansa.

Nigeria - Brennende Ölpipeline
Hoto: picture alliance/dpa/dpaweb

A yayin da shugaban Najeriya ya ba da umurnin ga jami’an tsaro su shawo kan masu kai hare-haren ga al'ummar kasar na cike da fatan ganin an samu aiwatar da kasafin kudin sau da kafa a dai lokacin da matsalolin tattalin arziki suka sanya kasar a gaba. Lamarin da kuma ya soma haifar da fargaba a zukatan al'ummar kasar

A lokutan baya dai masu tayar da kayar bayan na yankin Niger-Delta sun kasance wadanda suka gurgunta harkokin hako mai a yankin kafin a kai ga shirin afuwar da har yanzu ake aiwatar da shi. A yayin da aka ambato sun ba da sharudda na dakatar da kai hare-haren, za’a sa ido a ga yadda gwamnati zata bullo wa lamarin.