1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fadan taho mu gama a Senegal

Ibrahim SaniNovember 21, 2007
https://p.dw.com/p/CQ2s

Jami´an ´Yan sanda a Senegal sun harba barkonon tsohuwa cikin gungun masu zanga-zangar adawa da Gwamnati. Faɗan taho mu gaman tsakanin ɓangarorin biyu ya farune, bayan Gwamnati ta Umarci tashin masu saye da sayarwa, a bakin titunan babban birnin ƙasar ne wato Dakar. Rahotanni sun shaidar da cewa masu zanga zangar sun daddatse manya manyan hanyoyin birnin na Dakar tare da ƙone-ƙonen tayoyi. Hakan dai a cewar bayanai ya kawo tsaiko, a harkokin zirga zirgar sufuri a birnin na Dakar. A yanzu haka dai Jami´an ´ Yan sandan na ƙokarin shawo kan wannan al´amari.