1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU zata taimakawa rundunar zaman lafiya ta Afirka a Somalia

January 22, 2007
https://p.dw.com/p/BuTg

KTT ta yi kira da a gaggauta tura dakarun kiyaye zaman lafiya na kasa da kasa yankin Darfur mai fama da rikici dake yammacin Sudan. Ministocin harkokin wajen kungiyar EU sun fada a gun taron su na birnin Brussels cewa dole ne a hanzarta aiwatar da shirin kungiyar tarayyar Afirka da na MDD don girke rundunar zaman lafiya a lardin na Darfur. Amma a yanzu kungiyar EU zata ci-gaba da taimakawa rundunar kungiyar AU a wannan lardi har nan da watanni 6 masu zuwa. To sai dai ministocin ba su yi alkawarin ba da karin taimakon kudi ga wannan runduna ba. a lokaci guda kuma ministocin sun yi tir da tashe tashen hankula a yankin musamman lugudan wutar da jiragen saman yakin Sudan ke yi akan kauyuka.