Eu zata dauki mataki kan Turkiyya game da Cyprus
November 29, 2006Talla
Shugabar gwamnatin Jamus, Angela Merkel tayi maraba da matsin lambar da kungiyyar Eu kewa Turkiyya kann kasar Cyprus.
Angela Merkel, wacce ta shaidawa yan jaridu hakan a bayan fagen taron kungiyyar Nato, ta kara da nuna goyon bayan ta na daukar mataki, matukar Turkiyya taki amincewa da matakin kungiyyar ta Eu kann kasar ta Cyprus.
Kungiyyar ta EU dai na bukatar kasar ta Turkiyya bude tashohin ta na ruwa ne ga kasar ta Cyprus.
Kin yin hakan a cewar kungiyyar ta Eu, abu ne daka iya kaiwa ga datse tattaunawar shigowar kasar ta Turkiyya cikin yayan kungiyyar.