1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU: Za ta taimaka wa 'yan gudun hijira a Girka

Abdourahamane Hassane
July 27, 2017

Kwamitin zartaswa na Kungiyar Tarrayar Turai ya ba da sanarwa bullo da wani tsari na jin kai na taimaka wa 'yan gudun hijira da ke a kasar Girka.

https://p.dw.com/p/2hFnh
Griechenland Flüchtlingscamp Moria auf der Insel Lesbos
Hoto: Getty Images/AFP/L. Gouliamaki

Sabon tsarin wanda za a kashe kudade har Euro miliyan 209 kamar yadda babban kwamishina kungiyar ya bayyana zai taimaka wajen kyautata halin rayuwar masu neman mafaka. Wadanda ya ce a maimakon sauke su a gidajan bai daya zai ba da damar a rika daukar musu gidajan haya tare da daukar dauwainiyar su ta abinci da magunguna.