1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

EU ta karawa Iran wa´adin makonni biyu don kawo karshen shirinta na nukiliya

September 2, 2006
https://p.dw.com/p/Bukk

Ministocin harkokin wajen kasashen KTT sun amince su bawa Iran karin makonni biyu don ta bayyana matsayin ta na kawo karshen shirinta na nukiliya bayan da gwamnati a Teheran ta yi watsi da wa´adin MDD na dakatar da aikin inganta uranium. A kuma halin da ake ciki ministan harkokin wajen Jamus Franz-Walter Steinmeier a yau asabar yayi kira ga Iran da ta fito fili ta nuna cewa da gaske take wajen shiga shawarwarin akan dakatar da aikace aikacen ta na nukiliya. A wani labarin kuma shugaba Mahmud Ahmedi Nijad a yau asabar ya sake jaddada cewa Iran zata tsaya tsayin daka don kare manufofinta na shirin nukiliya a kowace irin tattaunawar da za´a yi akan wannan batu. Wadannan kalaman na shugaba Ahmedi Nijad sun zo ne gabanin ganawar da za´a yi a cikin mako mai zuwa tsakanin babban jami´in dake kula harkokin ketare na kungiyar EU Javier Solana da babban mai shiga tsakanin kan shirin nukiliyar Iran Ali Larijani.