1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Emmanuel Macron zai ziyarci Jamus

Yusuf Bala Nayaya
May 12, 2017

Zababben shugaban kasar ta Faransa Emmanuel Macron zai kai ziyararsa ta farko zuwa wata kasar waje, tun bayan zaben da aka yi masa a matsayin shugaban kasa.

https://p.dw.com/p/2cs0w
Deutschland Frankreich Merkel und Macron Kombobild
Hoto: Getty Images/AFP/T. Schwarz/J.-F. Monier

A yayin ziyarar tasa dai, sabon shugaban Faransan Emmanuel Macron zai tattauna da shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel a da nufin yin nazarin hanyoyin kara kulla alaka tsakanin kasashen biyu akan sababbin tsare-tsarensu, game da makomar kungiyar Tarayyar Turai. Wannan dai na zama ziyara ta farko da sabon shugaban kasar ta Faransa zai yi zuwa wata kasar waje tun bayan zabensa a matsayin shugaba a Faransan, ziyarar kuma da ke zuwa kwana guda bayan ya yi rantsuwar kama aiki. Faransa da Jamus dai su ake kallo a matsayin kashin baya ga kungiyar ta Tarayyar Turai tun bayan kafa kungiyar a shekara ta 1957.