Ehud Olmert ya nemi gafara ga Palestinawa
November 9, 2006Praministan ƙasar Isra´ila, Ehud Olmert, ya nemi gafara ga shugaban hukumar Palestinawa, a sakamakon hare-haren da rundunar Isra´ila ta kai, a zirin Gaza jiya laraba, wanda kuma su ka hadasa mutuwar mutane kusan 20.
A ta bakin Olmert, dakarun Isra´ila sun kai da wannan hari cikin kuskure.
Praministan Isra´ila, ya gayyaci Mahamud Abbas, zuwa tebrin shawarwari, domin samo bakin zaren warware wannan taƙƙadama da ta ƙi ci, ta ƙi cenyewa.
Budu da ƙari, ya ce a shirye ya ke, ya yi belin wasu, daga pirsinonin Palestinu ,da Isra´ila ta kama.
Kakakin Palestinu a Majalisar Ɗinkin Dunia, Ryad Mansur ya buƙaci komitin Sulhu ya hiddo sanarwar yin Allah ga Isra´ila, sannan ya tura rundunar shiga tsakani a yankin.
A ɗaya wajen kuma, an ci gaba da ganawa, tsakanin Mahamud Abbas, da Praminista Isama´il Hanniey, da zumar girka gwamnatin riƙwan ƙwarya.