1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dubban jama'a sun yi hijira daga Bangui

Salissou Boukari
September 26, 2017

Ofishin Majalisar Dinkin Duniya mai kula da harkokin jin kai OCHA, ya ce akalla mutane 23,000 suka gujewa matsugunnansu a biranen Bocaranga da na Niem da ke Arewa maso yammacin Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya.

https://p.dw.com/p/2kjzo
Zentralafrikanische Republik Kaga Bandoro Flüchtlingscamp
'Yan gudun hijiran Afrika ta TsakiyaHoto: picture-alliance/AP Photo/D. Belluz

Mafi yawan mutanen birnin Bocaranga 15,000 da na Niem 8,000 da ke iyaka da kasar Kamaru sun yi gudun hijira ne a cikin dazukan da ba za su iya samun taimako daga masu ayyukan agaji ba a cewar hukumar ta OCHA cikin wata sanarwa da ta fitar. A ranar Asabar ce dai mayakan 3R suka kai hari a birnin na Bocaranga, duk kuwa da kasancewar dakarun Majalisar Dinkin Duniya na MINUSCA a kasar.

Sa dai wata majiyar soja ta sanar da cewa lalle akwai mutanen da suka mutu, amma cikin yanayin da ake ciki yanzu akwai wahala a san adadin su da kuma na wadanda suka jikkata. Kungiyar ta 3R dai ta bullo ne a shekara ta 2015 a yankin Arewa maso yammacin kasar, inda take ikirarin bai wa al'ummar yankin kariya daga hare-haren 'yan Anti-Balaka.