Dole Turai ta daina yiwa Afirka kallon raini
June 10, 2007A yau ake kammala babban taron majami´ar Evangelika a birnin Kolon tare da wani kasaitaccen bukin addu´o´i. Wadanda suka shirya taron sun ce suna rai sama da mutane dubu 100 zasu halraci bukin addu´o´in na yau. Batutuwan da suka fi daukar hankali a taron na yini biyar sun hada da nuna adalci a huldodi tsakanin kasashen duniya, yaki da talauci sai kuma dangantaka tsakanin Kiristoci da Musulmi. A jiya asabar shugaban Jamus Horst Köhler da shugabar gwamnati Angela Merkel sun halarci gun taron. Dukkan ´yan siyasar biyu sun yi suka game da abin da suka kira girman kai da kasashen Turai ke yiwa Afirka. A jawabin da yayi shugaba Köhler yayi kira ga kasashen Turai da su yi aiki tukuru don yakar halayya irin ta ´yan mulkin mallaka.
“Dole ne mu saurari ´yan Afirka don mu gane bukatunsu da kuma burin da suke son cimma da kansu. Dole mu daina yi musu kallon raini.”
Ita kuma a nata bangare Angela Merkel cewa ta yi bai kamata Turai ta cusawa Afirka ra´ayoyin ta ba.