1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Daliban Afirka ta Kudu sun yi yajin karatu

Gazali Abdou TasawaOctober 19, 2015

Daliban jami'o'in Afirka ta Kudu na yajin daukar darasi tare da zanga-zanga domin nuna adawarsu da matakin karin kudin karatu da hukumomin jami'o'in kasar suka dauka.

https://p.dw.com/p/1GqeB
Studenten der African Leadership Academy
Hoto: DW / Gruntkowski

A Afirka ta Kudu, dubban dalibai na wasu jami'o'in kasar guda ukku sun shiga yajin daukar darasi dama gudanar da zanga-zanga domin nuna fushinsu kan tsadar kudin karatun a kasar. Wannan bore na dalibban ya tilasta wa hukumomin jami'o'in ukku da suka hada da jami'ar Rhodes ta garin Grahamstown da ke a Kudu maso Gabashin kasar da jami'ar birnin Cap da ke Kudancin kasar da kuma jami'ar Witwatersrand ta birnin Johannesburg dakatar da aikinsu.

Watanni kusan ukku kenan dai da daliban jami'o'n kasar ta Afirka ta Kudu ke gudanar da zanga-zanga lokaci zuwa lokaci domin tilasta wa hukumomin jami'o'in soke matakin kara farashin kudin karatu da sama da kashi goma daga cikin dari a shekara mai kamawa wanda suka ce ya na hana dalibai bakaken fata wadanda akasarinsu 'ya'yan talakawa ne damar shiga jami'a.