1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Dakarun Siriya sun kaddamar da farmaki a Aleppo

Suleiman BabayoOctober 16, 2015

Sojojin gwamnatin Siriya sun kaddamakar da farmaki samakaon samun tallafi daga jiragen saman yaki na kasar Rasha.

https://p.dw.com/p/1Gpak
Syrien Kämpfe zwischen IS und Rebellen bei Allepo
Hoto: Getty Images/AFP/Z. Al-Rifa

Dakarun kasar Siriya da ke samun rakiyar jiragen saman yaki na Rasha sun kaddamar da farmaki kan 'yan tawaye a kudancin birnin Aleppo da ke zama birni na biyu mafi girma a kasar. Wata kungiyar kare hakkin dan Adam ta ce dakarun gwamnatin Shugaba Bashar al-Assad ta kwace iko da wasu garuru biyu bayan jiragen saman yakin na rasha sun kai farmaki.

A wani labarin bincike kwararru na Majalisar Dinkin Duniya ya gano magoya bayan kungiyar IS da ke ikirarin neman kafa daular Islama suna bayar da kimanin dala dubu-10 domin samun masu Jihadi a kasashen Siriya da kuma Iraki. Galibin mayaka 'yan kasashen wajen sun fito ne daga Beljiyam.