1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan al-Shabab sun hallaka a harin kunar bakin wake

Yusuf BalaJune 21, 2015

Da fari al-Shabab ta ce ita ke da hannu wajen kai wannan harin da ta yi ikirarin cewa ya yi sanadin kashe mutane da dama a Somaliya.

https://p.dw.com/p/1FkP7
al-Shabaab Kämpfer in Somalia
Hoto: picture alliance / AP Photo

An ji karar wasu ababan fashewa sannan karar barin wuta na bindigogi a ranar Lahadin nan a tsakiyar baban birnin Mogadishu na kasar Somaliya.

Lamarin da ya faru a kusa da cibiyar bada horo ga jami'an leken asiri ta kasa kamar yadda wadanda su ka sheda lamarin su ka tabbatar wa da kamfanin dillancin labaran Reuters.

A cewar ma'aikatar harkokin cikin gidan Somaliya cikin dakarun na al-Shabab uku da su ka kai harin sun halaka, amma babu wanda harin ya ritsa da shi daga bangaren sojojin gwamnati.

Tuni dai kungiyar mayakan sakai ta al-Shabab ta ce ita ke da hannu wajen kai wannan harin da ya yi sanadin kisan mutane da dama a cewarta.