Cutar murar tsuntsaye ta kaseh wasu mata biyu a Indonesia
January 13, 2007Talla
Wasu mata biyu ´yan kasar Indonesia sun rasu sakamakon kamuwa da cutar murar tsuntsaye, wadda ta sake kunno kai kwanan nan a cikin kasar. Wani jami´in ma´aikatar kiwon lafiya ya ce daya daga cikin matan ta rasu a jiya juma´a yayin da dayar kuma ta cika da sanyin safiyar yau asabar. Dukkan su biyu ana yi musu jiya ne a wani asibiti dake Jakarta babban birnin kasar.