Cutar kwalara a kasar Benin
October 19, 2005Talla
Opishin ministan kiwan lahia na Benin, ya bayyana yaduwar cutar Kwalara a wannan kasa.
Annobar ta bullo tun watan july da ya wuce.
A halin da ake ciki, binciken da malluan kiwan lahia su ka gudanar, ya gano mutane 460 dasu ka kamu da cutar.9 daga cikin su, sun riga mu gidan gaskiya.
A karshen watan satumber da ya gabata, hukumar majalisar dinkin dunia, mai kulla da lahiyar al´umma, ta bayana damuwa a game da yaduwar annobar kwalara a kasashe 8 na yammacin Afrika, inda mutane dubu 46, su ka kamu da ita, wanda daga cikin su, 800 su ka kwanta dama.