Cigaba da ziyara Amr Musa a kasar Iraki
October 24, 2005Sakataran kungiyar hadin kan larabawa, Amr Musa na ci gaba da ziyara aiki a kasar Iraki.
Babban burin wannan ziyara, da ke gudana , kwanaki kalilan bayan gudanar da zabe, a game na kundin tsarin mulkin kasar Iraki, shine na samun goyan baya, daga al´ummomi daban daban, na kasa, domin shirya wani gagaramin taron hadin kai.
Ya zuwa yanzu, Amr Musa, ya samu goyan bayan da yan shi´a da kuma kurdawa mafi rinjaye a kasar Iraki.
Ya nuna matukar gamsuwa da bayanai, daga shugaban yan shi´a Ayatollah Ali Sistani, da kuma shugabanin kurdawa.
A yayin da ya yi rangadi a yankin Kurdistan, Amrr Musa ya gana da yan majalisar wakilai 111 na wannan yanki.
Wannan itace ziyara ta farko da wani shugaba balarabe ya kai a yankin tun bayan zaben wanan majalisa.
Babban abinda ke kawo cikas a halin yanzu, na shirya taron hadin kan kasar ,shine matsayin yan sunni.
Saidai wannan , ziyara na wakana a cikin yanayi hare haren kunar bakin wake kamar yada a ka saba kullum.
A ranar jiya, mutane 16 su ka rasa rayuka a fadin kasar baki daya.