1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Christian Kaboré ya yi rantsuwar kama aiki

Salissou BoukariDecember 29, 2015

Sabon shugaban kasar Burkina Faso wanda ya lashe zaben shugaban kasar na ranar 29 ga watan Nuwamba da ya gabata, ya yi kira ga 'yan kasar da su canza tunaninsu.

https://p.dw.com/p/1HVqB
Burkina Faso Präsidentschaftswahl - Gewinner Roch Kaboré
Hoto: Getty Images/AFP/I. Sanogo

Sabon shugaban kasar Burkina Faso Roch Marc Christian Kaboré ya yi rantsuwar kama aiki da tsakiyar ranar wannan Talatar, tare da halartar shugabannin kasashe da dama na Afirka da suka hada da na Côte d'Ivoire, Mali, Nijar, Sénégal, da na Guinea.

Wannan biki ya kawo karshen mulkin rikon kwarya da aka gudanar bayan faduwar gwamnatin shugaba Blaise Compaore a karkashin shugaba Michel Kafando wanda ya ce hakan wata babbar nasara ce ga demokaradiyya da 'yancin al'umma.

Dan shekaru 58 da haihuwa, sabon shugaban kasar ta Burkina Faso ya yi kira ga 'yan kasar da su dukufa wajen sauya halayyarsu, domin a samu cimma nasarar bunkasa kasar tare da karfafa ma'aikatunta, da ci gaban demokaradiyya da 'yanci al'umma.