1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

China ta zayyana mafita kan rikicin Myanmar

Yusuf Bala Nayaya
November 20, 2017

Shirin tsagaita wuta ta yadda 'yan gudun hijira a Bangaladash za su koma gida na daya daga cikin hanyoyi na warware rikicin Myanmara cewar mahukuntan Sin.

https://p.dw.com/p/2nuif
Aung San Suu Kyi Myanmar Wang Yi China
Hoto: picture-alliance/dpa/U Aung

Kasar China ta bayyana matakai uku da za su taimaka a kai ga samun mafita a rikicin kasar Myanmar da 'yan kabilar Rohingya ke ganin tasku, farawa da shirin tsagaita wuta ta yadda 'yan gudun hijira a Bangaladash za su koma gida. Ma'aikatar harkokin wajen kasar ta China ta bayyana haka gabannin tattaunawar jami'ai daga Tarayyar Turai da jami'ai daga yankin Asiya a zaman da za su yi a Myanmar ranar Litinin din nan.

Fiye da 'yan kabilar Rohingya dubu 600 ne suka tsallake zuwa Bangaladash tun a karshen watan Agusta bayan da sojoji suka kaddamar da farmaki a kansu a jihar Rakhine. Ministan harkokin wajen na China Wang Yi ya ce dole bangarorin biyu su zauna teburi guda kuma dole a samar da tsari na tsawon lokaci da zai kawar da talauci ga al'ummar yankin, talaucin da a cewar Yi ke zama tushen rikici tsakanin wadannan al'umma a kasar ta Myanmar.