1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Burundi ta kori 'yan Belgium

Ahmed SalisuNovember 20, 2015

Jam'iyya da ke mulki a Burundi ta bukaci 'yan kasar Belgiyum da su fice daga kasar bayan da suka zarge su da hada kai da 'yan adawa wajen rura wutar rikicin siyasa a kasar.

https://p.dw.com/p/1H9G5
Burundi Präsident Pierre Nkurunziza
Hoto: picture-alliance/dpa/C. Karaba

Jam'iyyar ta CNDD-FDD ta Shugaba Pierre Nkurunziza ta kuma ce 'yan kasar ta Belgiyum da ke zaune a Burundin na yunkuri ne wajen ganin an kawar da gwamnati mai ci daga gadon mulki.

To sai dai tuni 'yan Belgiyum din suka musanta wannan zargi. Gabannin wannan dai, a makon jiya gwmanatin Belgiyum ta shawarci 'yan kasarta da su fice daga Burundin din duba da yadda lamura ke ciga da dagulewa a kasar.