1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bukin samun shekaru 17 da sake haɗewar Jamus

October 3, 2007
https://p.dw.com/p/Bu9d
A yau tarayyar Jamus ke bukin cika shekaru 17 da sake hade yankin gabas wanda ya taba zama karkashin tsarin kwaminis da yammacin kasar. A daidai lokacin da ake wannan buki a yau batun harajin nan da ake yiwa lakabi da harajin zumunci wanda ma´aikata ke biya don sake gina gabashin kasar shi ya dauki hankalin jama´a. Ana dai yawaita yin kira da a soke wannan haraji na kashi 5.5 cikin 100 na albashin kowane ma´aikaci a nan Jamus. Daukacin ´yan siyasa na bangaren adawa sun goyi da bayan kawo karshen wannan haraji ko kuma a rage to amma ´ya´yan jam´iyar SPD na son a ci-gaba da biya. A cikin shekarun bayan nan an samu kwararar matasa daga gabashin zuwa yamacin kasar ta Jamus. Bincike yayi nuni da cewa kashi daya cikin 3 na mata matasa na shirin barin yankin gabashin suna masu cewa ba sa son tsarin rayuwa na yankin.