Boko Haram ta kashe manoma a Najeriya
September 8, 2017Talla
Mayakan Boko Haram sun halaka mutane takwas a wasu yankuna da al'ummarsu ke zama mafi rinjaye manoma a Arewa maso Gabashin Najeriya kamar yadda 'yan kungiyar kato da gora da mazauna yankunan suka fadawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP a wannan rana ta Juma'a.
Harin da aka kai wasu 'yan bindiga ne da ke tafe cikin motar daukar kaya sanfurin pick-up da baburan hawa suka kai shi a wajen birnin Maiduguri a ranakun Laraba da Alhamis.
Sun kuma kwace wa al'umma kayan abinci baya da sa wuta a kauyika uku da wasu a runbunan ajiyar kayan abincin, lamarin da ya sanya mutane suka gudu a cewar Ibrahim Liman shugaban sojan sakan na 'yan kato da gora.