1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Boko Haram ta kashe manoma a Najeriya

Yusuf Bala Nayaya
September 8, 2017

Wasu 'yan bindiga ne da ke tafe cikin motar daukar kaya sanfurin pick-up da baburan hawa suka kai harin a wajen birnin Maiduguri da ke jihar Borno a tarayyar Najeriya.

https://p.dw.com/p/2jbAe
Symbolbild Afrika Anbau Wasser
Hoto: Issouf Sanogo/AFP/GettyImages

Mayakan Boko Haram sun halaka mutane takwas a wasu yankuna da al'ummarsu ke zama mafi rinjaye manoma a Arewa maso Gabashin Najeriya kamar yadda 'yan kungiyar kato da gora da mazauna yankunan suka fadawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP a wannan rana ta Juma'a.

Harin da aka kai wasu 'yan bindiga ne da ke tafe cikin motar daukar kaya sanfurin pick-up da baburan hawa suka kai shi a wajen birnin Maiduguri a ranakun Laraba da Alhamis.

Sun kuma kwace wa al'umma kayan abinci baya da sa wuta a kauyika uku da wasu a runbunan ajiyar kayan abincin, lamarin da ya sanya mutane suka gudu a cewar Ibrahim Liman shugaban sojan sakan na 'yan kato da gora.