Bindige yaran uku da wasu ’yan bindiga daɗi suka yi a birnin Gaza, ya janyo fusatar shugabanin Falasɗinawa.
December 11, 2006Ɗimbin yawan jama’a da kuma shugabannin Falasɗinawa ne suke ta bayyana matuƙar ɓacin ransu game da bindige yara ƙanana guda uku, da wasu ’yan bindiga daɗi suka yi yau a birnin Gaza. Shugaban Falasɗinawa Mahmoud Abbas, ya ce kisan yaran, da wasu ’yan bindiga daɗin da ba a gano asalinsu ba tukuna suka yi, wato wani mummunan ɗanyen aiki ne na rashin imani da tausaya wa bil’Adama. Su dai yara ukun da aka bindige, masu shekaru tsakanin 6 da tara da haihuwa, duk ’ya’yan wani babban jami’in leƙen asirin Falasɗinawan ne mai biyayya ga shugaba Mahmoud Abbas. Dubban jama’a ne suka yi zanga-zanga a lokacin jana’izar yaran. Rahotanni sun ce wasu daga cikinsu ma sun kutsa cikin farfajiyar majalisar Falasɗinawan, inda suka yi ta buɗe wuta a kan ginin. Ɗaya daga cikin fararen hular da ke kusa da gun arangamar, ya rasa ransa a harbe-harben da aka yi, sa’annan wasu yara biyu kuma suka ji rauni, inji rahotannin. Kawo yanzu dai, babu wanda ya yi ikirarin ɗaukar nauyin harbe-harben, a daidai lokacin da ake ta ƙara samun hauhawar tsamari tsakanin ƙungiyar Hamas da ke jagorancin gwamnati da kuma rukunin Fatah ta shugaban Falasɗinawan, Mahmoud Abbas.