1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Barazanar kungiyar IS a kasar Libiya

Salissou BoukariFebruary 2, 2016

A yayin da ake kokarin kafa gwamnatin hadin kan 'yan kasa a Libiya, kungiyar IS reshen Libiya na kasancewa barazana ganin yadda take kaiwa ga arzikin man fetir.

https://p.dw.com/p/1Ho8R
Libyen Kämpfe gegen IS in Sirke
Hoto: picture-alliance/Photoshot/Hamza Turkia

Masu ikirarin jihadin na IS a Libiya dai da ke rike da birnin Syrte, na amfani ne da yanayin da kasar ke fuskanta na rashin tsayayyar gwamnati inda sau tari suka kai hare-hare ga ma'aikatun man kasar. Da yake magana kan wannan batu na kasar Libiya, sakataren harkokin wajen Amirka John Kerry da ke halartar wani zaman taro a birnin Roma na kasar Italiya, ya ce a daidai lokacin da ake daf da samun gwamnatin hadin kan 'yan kasa, bai kyautu ba a ce 'yan jihadin kasar ta Libiya sun kai ga samun biliyoyin dalar Amirka daga man da suke sata ba.