1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Barazanar barkewar cuta a sansanin 'yan Rohingya

Ramatu Garba Baba
September 22, 2017

Kungiyar likitocin agaji ta MSF ta baiyana takaici kan halin da 'yan gudun hijrar Rohingya ke ciki a kasar Bangladesh inda suke fuskantar barazanar barkewar cututtuka masu hadarin gaske.

https://p.dw.com/p/2kXg1
Rohyngia Krise Lebensmittel Versorgung
Hoto: Reuters/C.McNaughton

Kungiyar ta yi gargadin cewa dubban 'yan gudun hijrar na fuskantar barazana na barkewar cututtuka ganin yadda suke anfani da gurbattacen ruwa tare da zama cikin kazanta. Kungiyar ta ce baya ga ceto rayuwar wadannan mutane daga halaka akwai bukatar inganta rayuwar 'yan gudun hijra da ke tsugune a cikin tantunan don ba su taimako na kayyakin agaji da kuma tsaftace wurin zamansu.'Yan kabilar Rohingya fiye da dubu dari hudu ne suka tsallaka zuwa Bangladesh a sakamakon kisan da ake musu a kasarsu ta Myanmar sanadiyar rikicin da ya barke a watan Augusta.