1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bala'in fari a Somaliya

Usman Shehu UsmanFebruary 8, 2016

Sama da yara 58000 ke cikin hatsarin mutuwa sakamakon yunwa a kasar Somaliya domin baya ga yakin da kasar ke fama da shi akwai kuma matsalar karancin damina

https://p.dw.com/p/1Hrid
Flash-Galerie 60 Jahre Genfer Flüchtlingskonvention
Hoto: WFP/Rose Ogola7/picture alliance/dpa

A wani rahoton da MDD ta fitar yau Litinin 08.02.2016, tace sakamakon tsananin fari da aka yi, a yanzu kasar da yaki ya dai-daita, akwai wani bala'i da ke fisaknatarsu. A cewar rahoto tsananin rashin abinci mai gina jiki musamman ga yara kanana, a yanzu ya kai wani mizani na tada hankali. Inda yanzu yara sama da dubu 30 ke fama da bakar yunwa. Bisa kiyasin MDD, Somaliyawa miliyan hudu da dari bakwai, wato kashi arba'in na al'ummar kasar suna matukar bukatar tallafin abinci.