1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Bada tallafi ga fursunoni a Malawi

Ramatu Garba Baba
September 27, 2017

Halin da gidajen yarin kasar Malawi ke ciki abin takaici ne idan aka yi la'akari da hali na cunkoson fursunoni. Wannan ne ya sa wani matashi ya tashi tsaye don bai wa fursunoni tallafi ta hanyar samar musu mafita.

https://p.dw.com/p/2kodW
Afrika Gefängnis in Harare
Hoto: Columbus Mavhunga

Cunkoson mutane a gidan yarin kasar Malawi  inda fursunoni kan shafe shekaru ba tare da an yanke musu hukunci ba to rashin adalci ne a tsarin shari'a in ji Steve Sikwese daya daga cikin wadanda ke aikin samarwa fursunoni yanci karkashin wata kungiya mai zama kanta mai suna  Paralegal Advisory Service Institute (PASI) kungiyar ta na kai wa fursunonin ziyara tare da sauraron kokensu kafin daga bisani ta bi hanyar fitar da su daga gidan yarin,

Gefängnis in Afrika
Steve da kungiyarsa na kokari wajen ganin sun rage cunkoso a gidajen yarin MalawiHoto: picture-alliance/dpa/dpaweb

A cewar Steve, fursunonin da dama na daure ne saboda laifi na sace-sace wanda tsanannin talauci ya haddasa, in har sun duba sun kuma tabbatar laifin ba wani abun a zo a gani bane sai su shiga tsakani ta hanyar yin belinsu ko su  biya wa fursunonin kudin tara, amman wani abin takaici ma akwai fursunonin da ake tsare da su bisa zargi ba tare da an tabbatar da cewa sun aikata laifin ba, a cewar Steve wannan na daga cikin dalilan da ya sa shi da abokinsa Clifford Msiska kafa kungiyar ta PASI.

Mutane da dama ne dai suka ci gajiyar shirin da wannan kungiya ta PASI ke yi cikinsu kuuwa har da Philipina ta bar gidan yari a shekaru biyun da suka gabata. Namijin kokarin da wannan kungiyar ke yi ya sa an sami raguwar cunkoson fursunoni  a gidajen yarin kasar ta Malawi ganin yadda Steve da sauran abokan aikinsa suka yi nasarar taimaka wa dubban fursunoni samun yanci amman ta hanyar bin dokokin kasar da tsari na shari'a, bisa wadannan nasarori na kungiyar ta PASI wasu kasashen Afrika kamar su Uganda da Kenya sun soma yunkurin na aiki da wannan salo don tabbatar da adalci a kasa.