1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Armeniya: Za a koma tattaunawa da 'yan adawa

Yusuf Bala Nayaya
April 24, 2018

Jagororin mulki a Armeniya da 'yan adawa sun amince a koma teburin tattaunawa kamar yadda wani kusa a majalisar kasar ya bayyana a wannan rana ta Talata.

https://p.dw.com/p/2wZpw
Armenien Nikol Pashinyan Opposition
Nikol Pashinyan dan adawa a Armeniya na jan tawagar adawaHoto: picture-alliance/dpa/TASS/A. Geodakyan

Lamarin dai na zuwa biyo bayan zanga-zangar da ta yi awon gaba da kujerar firaminista kasar ta Armeniya. A wani sako da kafafan yada labaran kasar ta Armeniya suka fitar an jiyo mataimakin shugaban majalisa Eduard Sharmazanov na cewa a ranar Laraba ne za a fara tattaunawar. Serzh Sargsyan, wanda ya sauka daga mukamin firemiya a ranar Litinin, a baya ya yi mulki karkashin tsohuwar tarayyar Sobiyat tsawon kimanin shekaru 10 kafin kammala wa'adin mulkin a bana.