1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Arangama tsakanin dakarunTurkiyya da 'yan awaren PKK

June 19, 2012

Sojoji fiye da 20 su ka mutu lokacin arangamar da a ka gwabza tsakanin kurdawa da sojojin gwamnatin Turkiyya

https://p.dw.com/p/15I2j
ARCHIV - Türkische Soldaten sichern die Gebirgsregion in Hakkari (Nordtürkei) an der Grenze zum Irak (Archivfoto vom 26.10.2007). Türkische Soldaten sind bei einem Einsatz gegen die verbotene Kurdische Arbeiterpartei PKK in das Nachbarland Irak eingedrungen. Die Aktion sei am Vorabend begonnen worden und richte sich gegen Lager der PKK im Norden des Irak, teilte der Generalstab am Freitag (22.02.2008) mit. Vorher habe es bereits Angriffe der türkischen Luftwaffe gegeben. Die türkische Armee teilte weiter mit, der Einsatz von Bodentruppen im Irak solle so schnell wie möglich wieder beendet werden. Die PKK hat aus den Kurdengebieten im Irak mehrfach tödliche Angriffe auf türkische Truppen gestartet. Foto: str +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: Picture-Alliance/dpa

An gwabza wani ƙazamin faɗa, tsakanin dakarun gwamnatin Turkiyya, da sojojin aware na ƙurdawa, a yankin Hakkari dake kan iyakokin Turkiyya da Iraki.

Wannan shine faɗa mafi muni da ɓangarorin biyu suka gawbaza tun farkon shekara da muke ciki.

Sojoji Takwas na gwamnatin Ankara sun rasa rayuka, sannan kusan 20 suka ji raunuka, a yayin da ƙurdawan suka yi asara dakaru 10.

Wannan faɗa ya ɓarke bayan da dakarun awaren PKK, suka kaiwa wasu sojojin gwamnati farmaki, kamin daga bisani su arce cikin tsaunukan yankin Kurdistan.

Daga lokacin da PKK ta ɗauki makamai a Turkiyya a shekara 1984 zuwa yanzu, aƙalla mutane dubu 40 suka rasa rayuka a cikin arangama da dakarun gwamnati.

Turkiyya da Amurika da kuma ƙasashen ƙungiyar Tarayya Turai ,na ɗaukar ƙungiyar aware ta PKK a matsayin ƙungiyar ta'adanci.

Mawallafi: Yahouza Sadissou Madobi
Edita: Umaru Aliyu