1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Annan ya yi kira ga Falasdinawa da su fita kada kuri´a

January 22, 2006
https://p.dw.com/p/BvBB

Babban sakataren MDD Kofi Annan yayi kira ga Falasdinawa da su fita kwansu da kwarkwatansu don kada kuri´a a zaben ´yan majalisar dokokin da za´a yi a ranar laraba mai zuwa. A cikin wata sanarwa da ya bayar Annan ya ce zaben na matsayi wani muhimmin mataki a tarihin doguwar gwagwarmayar da al´umar Falasdinawa ke yi. Annan ya yi fatan cewa zaben zai bude hanyar samar da zaman lafiya mai dorewa a wannan yanki. Tun dai a jiya asabar jami´an tsaron Falasdinawa kimanin dubu 60 suka fara kada ta su kuri´ar, don ba su damar tabbatar da tsaro a lokacin zaben na ranar 25 ga watan nan na janeru.